A Yau S02 Episode 2 (Illar Zina) Lyrics
- Genre:Afrobeats
- Year of Release:2021
Lyrics
A Yau S02 Episode 2 (Illar Zina) - Fresh Emir
...
Aku me bakin magana
Ayau ma nazo zanyi magana
Ayau magana...Ayau da magana
Ayau da magana!
Fresh emir nazo na ma tambayoyi
Nasan zaka ban amsa cikin zafi ko ruwan sanyi!
Me al'ummar mu suka duƙufa suna yi..? Kuma cutar da goben su suke yi!
Toh abu na farkon sa shine shaye-haye!
A 'Ayau' season one, episode seven nayi kiranye!
Harna bayyana haukane makomar me shaye-shaye!
Abu ba biyunsa zinace-zinace ina na tuna wannan na kan rasa me zance?
Don wannan al'amari ya ƙazance
Yakai matakin da yafi kwatancen duk me kwatancen!
Kaga! Wannan musifa baga Yara ba, baga manya ba, baga tsofaffin ba!
Maganar gaskiya mun saki Allah!
Wannan ne yasa kullum muke kwalla
Kaga yanzu har lasisi ake yiwa fasiƙanci
Kome kayi babu wani kyakkyawan hukunci
Wannan musiba ubangiji kayi mana sassauci
Da farko zan fara kiran matasa
Waɗanda suka ɗauki zina gaasa
Yasan hakan na sanya nisa ga ubangijin sa
Sannan zai wahala ɗorawar arzikinsa
Don baya taimakawa uwansa sai karuwar sa
To taya Allah zai albarkacesa?
Sai kaga uwamsa na fama kan dari biyu
Yaba karuwarsa dubu goma
Yakan iya sayawa yar iska shawarma
Allah Sarki uwar da haifeshi ita ko loma
Ya kai yar iska tayi kwanan asi
Mama ga zafi, ga sauro, ga jakarta babu ko sisi
Baka taimakon uwa da yan uwa
Babu me cin kuɗin ka sai me hotel, karuwa.
Zaido me yin wannan hali ya daina, in karuwace kanai mata tana kallonka Wawa.
Idan ta tatsa yau gobe ta tura kawa jibi tura kawa...
Tunda kaƙi yiwa uwa
Bari yanzu na juya akalata
Gurin magidantan dake da mata
Ko tanbadaddiyar matar dake da mijinta
Ga wadatar ta ga lafiyar ta amma take bin kwarata
Me gida bari na fara ta kanka
Don naga kai kafi kowa ma hauka
Kanada mata daya, biyu, uku dan hauka me yasa kake so in ka mutu wuta zaka?
Ga matar ka komai kayi lada za'a baka
Amma rashin tunani irin naka har wata macen banza a waje zata ruɗeka?
Mata kuna ina ? Na juyo kanku kuma
Me gidan ki yana can ya tafi nema
Wani kasuwanci yake wani dakoma
Amma kike cimai amana kamar kura da nama
Malamai na wa'azi kinaji wuta zaki kema
Abin takaicin kaga har tsofaffi
Yabi uwa, ya bi ya, ya bi jika kaji tsohon wofi
Ba tsoron Allah shiya sa musifu ke kara karfi
In ka shiga inuwa ta ƙonaka rana ma zafi
Aku mai bakin magana...Ayau na zo na gama magana...